Gwamnatin jihar Legas ta kama mutane 46 saboda yin bahaya a fili

Gwamnatin jihar Legas ta kama mutane 46 saboda yin bahaya a fili

Gwamnatin Jihar Legas ta ƙara ƙarfafa hukunta masu yin bahaya a fili, inda ta kama mutane 46 a sabon aikin sintiri da aka gudanarwa a manyan titunan kasuwanci na Tsibirin Legas.

Hukumar ta aiwatar da kamun ne ta hanyar rundunar yaƙi da yin bayan gida a Fili ta Jihar Legas a safiyar wannan makon, inda aka mayar da hankali kan wuraren da aka gano rashin tsaftar muhalli, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin da ake yi na aiwatar da dokokin muhalli da kare lafiyar jama’a.

Daraktan gudanarwa kuma shugaban hukumar Kula da shara ta Legas, Dr. Muyiwa Gbadegesin, ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin hukuma na gwamnatin jihar a ranar Talata.

Sanarwar ta ce, “Gwamnatin Jihar Legas, ta hanyar Rundunar Yaki da Yin Bayan Gida a Fili, ta kama maza da mata 46 masu laifi a yayin wani aikin sintiri da aka tsara da aka gudanar a safiyar yau a fadin Tsibirin Legas.”

Comments

Popular posts from this blog

Pathway to Purpose Initiative Strengthens Community Outreach with NDLEA Partnership, Hospital Support in Zaria

Pathways to Choice Project Targets Improved Literacy for Girls in Kaduna Communities

KANO REJOICES AS GOVERNOR ABBA YUSUF NOMINATES GARO FOR DEPUTY GOVERNOR